By using this site, you agree to the Privacy Policy and Terms of Use.
Accept
Danfako Media Ventures Danfako Media Ventures
  • Home
  • News
    • Politics
    • Crime
  • Sport
  • Interviews
  • Opinion
  • Health
  • Features
  • Advert
  • Contact
Reading: GWAMNATIN JIHAR KADUNA TA SAKA DOKAR HANA FITA A YANKIN CHIKUN
Share
Notification Show More
Font ResizerAa
Font ResizerAa
Danfako Media Ventures Danfako Media Ventures
Have an existing account? Sign In
Follow US
© 2022 Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Danfako Media Ventures > Blog > Daily News > GWAMNATIN JIHAR KADUNA TA SAKA DOKAR HANA FITA A YANKIN CHIKUN
Daily News

GWAMNATIN JIHAR KADUNA TA SAKA DOKAR HANA FITA A YANKIN CHIKUN

danfako
Last updated: 2023/04/03 at 5:14 PM
By danfako 3 Min Read
Share
SHARE

Wata sanarwa da Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Ciki Gida ta jihar ta fitar a ranar Litinin ta ce an dauki matakin saka dokar ne sakamakon karya doka da oda da aka yi da suka jawo kisan wasu mutum biyu a yayin wani rikici.

Gwamna Nasir El-Rufai ya yabi jami’an tsaro kan kokarin dakile rikicin da gaggawa tare da yi wa iyalan wadanda suka rasu ta’aziyya/ Hoto Nasir El Rufai Facebook
Gwamnatin Jihar Kaduna a arewa maso yammacin Nijeriya ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’a 24 a yankin Sabon Garin Nasarawa-Tirkaniya da ke karamar hukumar Chikun.

Wata sanarwa da Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Ciki Gida ta jihar ta fitar a ranar Litinin ta ce an dauki matakin saka dokar ne sakamakon karya doka da oda da aka yi da suka jawo kisan wasu mutum biyu a yayin wani rikici.

“An umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da dabbaka dokar hana fitar a yankin, don mayar da al’amura daidai, a yayin da ake ci gaba da bincike.”

Sanarwar ta kuma umarci al’ummar yankin da su tabbatar sun bi dokar sau da kafa wacce ta fara aiki ba tare da bata lokaci ba.

A wata sanarwar ta daban kuma, gwamnatin Jihar Kadunan ta haramta duk wasu harkoki da ke da alaka da rikcin da aka samu a al’ummomin Nasarawa da Sabon Garin Nasarawa na yankin Chikun din.

Tuni aka kama mutum uku da ake zargin su da hannu a kisan mutanen biyu da aka yi sakamakon rikicin da ya barke a wajen.

“Gwamnatin Jihar Kaduna ta haramta duk wasu harkoki masu alaka da rikicin da ya faru ranar Lahadi da daddare da ya yi sanadin mutwar mutum biyu tare da jikkata mutum shida a Sabon Garin-Tirkaniya da ke karamar hukumar Chikun,” in ji sanarwar.

Tuni aka kai wadanda suka jikkata asibiti don duba lafiyarsu in ji sanarwar.

Ta kara da cewa an dauki matakin ne bayan da aka karbi cikakkun bayanai na tsaro daga wajen sojoji da ‘yan sanda da hukumar tsaro ta farin kaya da kuma ganawar gaggawa da aka yi da shugabannin addini da masu masarautu a Kaduna.

Cikin al’amuran da aka hana gudanarwa din sun hada da Kidan Bishi da Kidan Gala da Farauta.

Kazalika gwamnati ta bayar da umarnin kama duk wani da aka kama da alaka da safarar miyagun kwayoyi a Nasarawa and Sabon Garin Nasarawa.

Gwamna Nasir El-Rufai na jihar ya yabi jami’an tsaro kan kokarin dakile rikicin da gaggawa tare da yi wa iyalan wadanda suka rasu ta’aziyya, yana mai jaddada cewa za a yi bincike sosai.

You Might Also Like

WE’LL MAKE BADMINTON MORE COVENTIONAL, ATTRACTIVE AND STRONGER IN NIGERIA KOLO JIBRIN MAMMAN SEC. GEN. ABCIN

SEN YARI BAGS BABA ISALE OF IKORODU KINGDOM TITLE

BANDITS KILLS APC CHIEFTAIN IN ZAMFARA

I’ll provide more assistance in Yobe in 2026 – KMT

KMT declares for governorship promises a better Yobe 

Share This Article
Facebook Twitter Email Print
Previous Article BREAKING: BANDITS KIDNAPPED TWO FUG FEMALE STUDENTS IN ZAMFARA
Next Article DANFAKO MEDIA VENTURES FELICITATES WITH ZAMFARA PPRO
Leave a comment

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Stay Connected

Facebook Like
Twitter Follow
Youtube Subscribe
Telegram Follow
- Advertisement -
Ad image

Latest News

WE’LL MAKE BADMINTON MORE COVENTIONAL, ATTRACTIVE AND STRONGER IN NIGERIA KOLO JIBRIN MAMMAN SEC. GEN. ABCIN
Daily News Interviews News Sport
SEN YARI BAGS BABA ISALE OF IKORODU KINGDOM TITLE
Daily News News
BANDITS KILLS APC CHIEFTAIN IN ZAMFARA
Crime Daily News News
I’ll provide more assistance in Yobe in 2026 – KMT
Daily News News Politics
//

We influence 20 million users and is the number one business and technology news network on the planet

Sign Up for Our Newsletter

Subscribe to our newsletter to get our newest articles instantly!

[mc4wp_form id=”55″]

© 2022 Foxiz News Network. Ruby Design Company. All Rights Reserved.
Join Us!

Subscribe to our newsletter and never miss our latest news, podcasts etc..

[mc4wp_form]
Zero spam, Unsubscribe at any time.
Welcome Back!

Sign in to your account

Lost your password?